Isa ga babban shafi
Jamhuriyar Congo-Zabe

Congo:Gwamnati ta yi wa shugabannin Kataloki kashedi

Kawancen jam’iyyun da ke mara wa gwamnati baya a Jamhuriyar Dimokuradiyyar Congo, sun zargi shugabannin mujami’ar katolika da yin shisshigi a cikin lamurran siyasa, bayan da majalisar koli ta Katolikan ta yi ikirarin cewa ta san wanda ya lashe zaben shugabancin kasar.

Corneille Nangaa, shugaban hukumar zaben Jamhuriyyar Dimokuradiyyar Congo.
Corneille Nangaa, shugaban hukumar zaben Jamhuriyyar Dimokuradiyyar Congo. © JOHN WESSELS / AFP
Talla

Jam’iyyun kawance da ke mara wa gwamnatin sun bayyana ikirarin da shugabannin addinan suka yi da cewa ya yi hannun riga da matsayinsu na iyayen al’umma.

A jiya juma’a Kwamitin Tsaron MDD ya gudanar da zama na musamman dangane da halin da ake ciki a Congo, to sai dai an tashi ba tare da fitar da wata sanarwa ba saboda bambancin ra’ayi a tsakanin manyan kasashen duniya kan halin da ake ciki a kasar.

A gobe lahadi ne ya kamata a fitar da sakamakon zaben shugabancin kasar ta Congo, to sai dai hukumar zabe ta ce abu ne mai yiyuwa a dage ranar, yayin da ‘yan adawa ke cewa ana neman murda sakamakon ne.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.