Isa ga babban shafi
Jamhuriyar Congo

An yi wa fursunoni 700 afuwa a Jamhuriyar Dimokuradiyyar Congo

Sabon shugaban Jamhuriyar Dimokuradiyyar Congo Felix Tshisekedi ya rattaba hannu kan kudurin doka da ke bayar da izinin sakin fursunonin siyasar kasar, daya daga cikin alkawurran da ya dauka cikin jawabin rantsar da shi.

Shugaban Congo, Félix Tshisekedi a taron Tarayyar Afirka, 2019-02-10
Shugaban Congo, Félix Tshisekedi a taron Tarayyar Afirka, 2019-02-10 SIMON MAINA / AFP
Talla

Babban jami’in gwamnati a fadar shugaban Vital Kamerhe, shi ne ya bayar da haske dangane da wannan mataki, inda ya ce daga cikin wadanda aka yi wa afuwar har da wasu sanannun ‘yan adawa wato Firmin Yangambi da Franck Diongo.

A jimilce fursunonin siysa 700 ne wannan mataki ya shafa a sassa daban daban na kasar, kuma ana iya sallamar su daga gidajen yari kowane lokaci daga yau alhamis.

Sakin fursunonin siyasa, na daga cikin muhimman bukatun da ‘yan adawa suka gabatar wa tsohon shugaba Joshep Kabila tun shekara ta 2016, kafin daga bisanin Tshisekedi wanda tsohon dan adawa ne ya dauki wannan alkawari lokacin da yake jawabi a ranar da ya karbi ragamar mulkin kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.