Isa ga babban shafi
Wasanni

Ghana na neman 'yan Najeriya 3 kan zargin garkuwa da Jakadan Estonia

Rundunar ‘yan sandan Ghana ta yi shelar neman wasu ‘yan Najeriya 3 da ake zargi da sace Jakadan Estonia a kasar Nabil Makram Basbous.

Wasu jami'an 'yan sanda a Ghana
Wasu jami'an 'yan sanda a Ghana Daniel Finnan
Talla

Rundunar ‘yan sandan Ghanan wadda ta yi nasarar ceto Mr Nabil da masu garkuwar suka sace da safiyar Alhamis din da ta gabata, ta ce ‘yan bindigar mutum 3 ‘yan Najeriya ne.

Cikin sanarwar da Kakakin rundunar Efia Tenge ya fitar, ya ce an sace Mr Nabil mai shekaru 61 ne lokacin da ya ke tsaka da tattaki kamar yadda ya saba kowacce safiya a kewayen unguwarsa.

Sanarwar ta ce har zuwa lokacin da ta yi nasarar ceto Jakadan Estoniyan a Ghana, ba ta iya gano wajen da ‘yan bindigar su ke ba.

Rundunar ‘yan sandan dai ba ta bayyana sunan mutanen 3 haka zalika ba ta bayyana hotunansu ba, sai dai ta tabbatar da cewa ‘yan Najeriya.

 

 

 

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.