Dan kunar bakin wake ya kashe mutane 13 a Somalia
Akalla mutane 13 suka mutu a garin Beledweyne da ke tsakiyar kasar Somaliya a ranar Asabar, bayan da wani dan kunar bakin wake ya tarwatsa kansa a wani gidan cin abinci da shaidu suka ce cike yake da jami'an gwamnatin yankin da sauran 'yan siyasa.
Wallafawa ranar:
Tuni kungiyar al-Shabaab ta dauki alhakin kai harin, day a jikkata wasu mutane 18, baya ga rayukan day a lakume.
Cikin makwanni biyun da suka gabata, sai da kungiyar ta Al Shebaab ta kai wasu hare-haren kashi biyu a sassan kasar Somalia.
Jami’an ‘yan sanda da na gwamnati sun tabbatar da harin kunar bakin waken da aka kai gidan cin abincin, amma ba su bayyana adadin wadanda suka mutu ba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu