Isa ga babban shafi

Algeria ta kaddamar da Masallaci mafi girma a Afrika

Shugaban Algeria Abdelmadjid Tebboune, a hukumance ya bude babban Masallacin kasar, wanda shi ne Masallaci na uku a yanzu mafi girma a duniya kuma na daya a nahiyar Afirka.

Algeria ce kasa ta farko da ke dauke da katafaren masallaci a wajen biranen Makka da Madina.
Algeria ce kasa ta farko da ke dauke da katafaren masallaci a wajen biranen Makka da Madina. © AF
Talla

Katafaren masallacin da zai iya daukar masallata dubu 120 a lokaci guda, an fara gudanar da sallah a cikinsa ne a watan Oktoban 2020, a lokacin shugaban kasar ke fama da cutar Covid-19 da ta hanashi halarta.

Masallachin da ake kira da Great Mosque of Algiers, na da hasumiya mafi tsayi a duniya, inda ta kai mita 265 kwatan-kwacin kafa 869.

Wani bangare na katafaren Masallacin da Algeria ta gina.
Wani bangare na katafaren Masallacin da Algeria ta gina. © AF

An kwashe sama da shekaru 7 ana aikin gina shi, kuma an yi amfani da kadada 27.75 wajen tsara ginin masallacin.

A cikin Masallacin, akwai filin saukar jirgi mai saukar ungulu da kuma katafaren dakin karatu da zai iya daukar litattafai har miliyan daya.

A yanzu Algeria ce kasa ta farko da ke dauke da katafaren Masallaci a wajen biranen Makka da Madina, kuma ana sanar al'ummar musulmi za su yi amfani da masallacin wajen gudanar da ibada a lokacin azumin watan Ramadan.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.