MDD ta tabbatar da barkewar cutar kwalara a Syria
Hukumar kula da Lafiya ta Majalisar Dinkin Duniya, ta ce akalla mutane 10 aka tabbatar da mutuwarsu sakamakon barkewar cutar kwalara.
Wallafawa ranar:
Hukumar ta ce yanzu haka karin wasu mutane 12 suna fama da cutar.
Rabon samun bulluwar wannan cuta a kasar Syria tun a shekarar 1999 wacce ake tunanin za ta iya yaduwa zuwa wasu sassan kasar.
Masu bincike a fanning kiwon lafiya sun ce mai yiwu mayakan dake fada da gwamnatin Shugaba Bashar al Assad ne suka shiga kasar da kwayoyin cutar.
Har ila yau hukumar ta bayyana samun burbushin kwayar cutar polio a jikin wasu yara kanana.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu