Isa ga babban shafi
Myanmar

Jam’iyyar Suu Kyi na kan gaba a zaben Myanmar

Wani Jigo a Jam’iyyar da ke mulkin kasar Myanmar ya ce sun sha mummunan kaye a hannun jam’iyar adawa ta Aung San Suu Kyi yayin da ake ci gaba da tattara sakamkon zaben kasar.

Aung San Suu Kyi shugabar Jam'iyar adawa ta LDP a Myanmar
Aung San Suu Kyi shugabar Jam'iyar adawa ta LDP a Myanmar REUTERS/Jorge Silva
Talla

Sakamakon farko ya nuna cewar Jam’iyar Suu Kyi ta NLD ta lashe kujeru 49 daga cikin 54 da aka sanar, kuma jam’iyar na neman kashi 67 ne dan samun rinjaye a Majalisar.

Wani babban jami’in jam’iya mai mulki Kyi Win ya shaidawa kamfanin dillancin labaran Faransa cewar sun fadi kasa warwas a zaben.

An ruwaito Suu Kyi na bayyana fatar samun rinjaye a zaben da aka gudanar a ranar Lahadi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.