Isa ga babban shafi
Myanmar

An rantsar da Kyaw shugaban kasar Myanmar

An rantsar da Htin Kyaw a matsayin sabon zababben shugaban kasar Myanmar, abinda ya kawo karshen mulkin sojin kasar da aka kwashe tsawon shekaru a na yi.

Sabon shugaban kasar Myanmar Htin Kyaw.
Sabon shugaban kasar Myanmar Htin Kyaw. STR / AFP
Talla

Bikin na yau mai dimbin tarihi ya kawo karshen shekaru 50 da aka kwashe ana mulkin soji sakamakon nasarar da Jam’iyyar NLD ta Aung San Suu Kyi ta samu a karkashin sauyin da shugaba Thein Sein ya kaddamar.

Thein Sein wanda ya hau karagar mulki sakamakon zaben shekarar 2011 ya kaddamar da sauye-sauye saboda sukar da kasar ta fuskanta da kuma takunkuman da kasashen duniya suka kakaba ma ta.

Sabon shugaban ya samu kuri’u 360 daga cikin 652 a zauren majalisar inda ya kayar da mutane biyu wadanda yanzu za su zama mataimakan shugaban kasa.

Sabon shugaban mai shekaru 69 ya yi karatu a Birtaniya kuma an ma sa shaidar cewar yana kamanta gaskiya da kuma biyayya kuma ana sa zai yi aiki a karkashin Aung San Suu Kyi wadda kundin tsarin mulkin Myanmar ya hana ta zama shugaban kasa.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.