Isa ga babban shafi
Syria

Dakarun Turkiya sun daura tutar kasar a tsakkiyar birnin Afrin

Shugaban kasar turkiya Recep Tayyip Erdogan a yau lahadi ya bayyana cewa, mayakan Syriya dake samun goyon bayan gwamnatin Ankara sun yi nasarar kwace daukaci yankin tsakkiyar birnin 'Afrin, tingar mayakan kurdawa a yankin arewa maso yammacin kasar Syriya.

Dakarun turkiya a garin Afrin na Syriya bayan kama yankin tsakkiyar birnin  Maris 18, 2018
Dakarun turkiya a garin Afrin na Syriya bayan kama yankin tsakkiyar birnin Maris 18, 2018 Reuters/路透社
Talla

Afrin dai ya kasance birnin dake fuskantar hare haren daga sojan Turkiya tun a ranar 20 ga watan Janairun da ya gabata, a kokain da kasar ke yi wajen ganin ta fatatakar dakarun sa kan kurdawa na kungiyar (YPG).

Rundunar sojan kasar ta Turkiya dai, a kan shafinta na Twitter ta watsa wani hoton videon dake nuna sojanta na rataya wata tutar kasar a wata barandar bene

Gwamnatin Ankara dai, na kallon kungiyar YPG ta kurdawa a matsayin kungiyar yan ta’adda, duk da cewa, dakarun kurdawan na samun nasu goyon baya ne, daga kasar Amruka, domin su yaki masu ikrarin jihadi na kungiyar ISIS a Syriya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.