Isa ga babban shafi
India-Ta'addanci

Kotun India ta zartas da hukuncin kisa kan mutane 38 saboda harin 2008

Kotun India ta zartas da hukuncin kisa kan wasu mutane 38 yau juma’a wadanda ke da hannu a harin bom din shekarar 2008 da ya kashe gomman jama’a a yammacin birnin Ahmedabad na kasar.

Zaman shari'ar mutanen 28 da kotu ta zartaswa hukuncin kisa dangane harin 2008 a birnin Ahmedabad.
Zaman shari'ar mutanen 28 da kotu ta zartaswa hukuncin kisa dangane harin 2008 a birnin Ahmedabad. Sam Panthaky AFP
Talla

Tun a ranar 8 ga watannan ne kotun ta birnin Gujarat cibiyar kasuwancin India ta samu mutane 49 da hannu a kaddamar da farmakin na 2008 wanda ya kashe mutane 56 amma kuma yayin zaman kotun na yau juma’a mai shari’a A R Patel, ya zartas da hukuncin kisa kan mutane 38 daga ciki.

Babban mai shiri'ar Amit Patel ya ce sauran mutum 11 cikin masu hannu a farmakin 49 an yanke musu hukuncin daurin rai da rai a gidan yari.

 Wata kungiya da ta kira kanta da mujahidin India ta dauki alhakin farmakin na shekarar 2008 wanda ta ce fansa ce kan rikicin 2002 a birinin na Ahmedabad da ya kashe musulmi kusan dubu guda.

Akalla mutane 80 aka fara tuhuma da hannu a farmakin na 2008 amma kuma Mr Patel ya ce tuni aka wanke wasu 28 yayinda sauran kusan kowannensu aka same shi da ko dai laifin kisan kai ko hannu a taimakon ayyukan ta’addanci.

Kusan shekaru 10 baya ne aka faro shari’ar wadda ta akalla mutane dubu 1 da 100 ke bayar da shaida gabanin kammala ta a yau juma’a.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.