Isa ga babban shafi

Dalibai 19 sun mutu a wani hari da aka kai cibiyar zana jarabawa a Afghanistan

Akalla mutane 19 suka mutu galibinsu mata a wani harin kunar bakin wake da aka kai wata makaranta a birnin Kabul dai dai lokacin da daliba ke rubuta jarabawa.

Harin ya faru ne a lokacin da yara ke tsaka da rubuta jarabawar shiga jami'a.
Harin ya faru ne a lokacin da yara ke tsaka da rubuta jarabawar shiga jami'a. AP - Rahmat Gul
Talla

Majiyar tsaron birnin na Kabul fadar gwamnatin Afghanistan ta ce dandazon matasan da ke kokarin shiga jami’a ne su ke tsaka da rubuta jarabawa a cibiyar ta Kaaj, wajen da aka kai farmakin.

Wani matashi, da ya bayyana sunansa da Akbar dalibi a cibiyar shirya jarabawar shiga jami’ar ta Kaaj, ya ce sun kai kimanin 600 wadanda ke zana jarabawar amma galibin wadanda harin ya rutsa da su mata ne.

Asibitin da aka garzaya da wadanda suka jikkata. aharin nay au juma’a sun ce, yanzu haka sun karbi gawarwakin mutane 19 galibisu mata yayinda ake da dalibai masu tarin yawa da suka jikkata.

Harin dai ya faru ne a yankin Dasht-e-Barchi da ke makwabtaka da yammacin Kabul mai rinjayen mabiya shi’a, wato dai yankin da ke matsayin gid aga tsirarun kabilar Hazara.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.