India: A kalla mutane 24 sun rasa rayukansu sakamakon ruwan sama
A kalla mutane 24 ne suka rasa rayukansu a Indiya, wadanda suka hada da guda 9 da suka rasa rayukansu, karkashin rugujewar da wani ginin da ake gudanar da bautar addini a cikinsa ya yi, a yayin da wasu gomman mutane kuma suka bata, bayan sakar ruwan sama mai yawa, da ya haifar da ambaliya tare da zaftarewar kasa, a cewar mahukumta.
Wallafawa ranar:
Mamakon ruwan da aka kwashe tsawon kwanaki ana yi, ya ruguza gadoji da kuma gidajen zaman jama’a, tare da yin awan gaba da motoci a jihar Uttarakhand da Himachal Pradesh, dake arewacin kasar.
Duk dai a wannan lokaci na markar damina, ambaliyar ruwa da zaftarewar kasa sun kasance a kullum masu haifar da katafariyar barn aga dukiya da rayukan jama’a. a cewar masana, ruwan na marka na ci gaba da yawa a ko wane lokaci sakamakon sauyin yanayin da duniya ke fuskanta.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu