Isa ga babban shafi
Eritrea-MDD

MDD ta kakubawa Eritrea takunkumi

Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya kakubawa kasar Eritrea sabbin takunkumi, saboda zargin da ake mata na taimakawa kungiyar Al Shabab, tare da goyon bayan harin ta’addanci.

Taswirar kasar Eritrea
Taswirar kasar Eritrea @Google
Talla

Kasashe 13 daga cikin 15 da ke Majalisar suka amince da takunkumin, sai dai kasashen Rusha da China suka kauracewa Majalisar.

Bukatar Najeriya da Gabon na ganin an hana masu zuba jari a ma’adinan kasar da kuma hana ‘Yan kasar da ke zama a kasashen duniya aikawa da kudi gida, bai samu goyan baya ba a Majalisar.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.