Isa ga babban shafi
Fadar Vatican

Paparoma Francis na ziyara a kasashen Gabas ta Tsakiya

Jagoran mabiya mujami’ar Katolika na Duniya Paparoma Francis na daya, a yau asabar ya isa kasar Jordan, wato matakin farki na ziyarar kasashen yankin Gabas ta Tsakiya da zummar kara samar da hadin kai tsakanin mabiya addinan Kirista, Yahudawa da kuma Musulmi.

Paparoma Francis na daya a ziyarar da ya kai kasar Jordan
Paparoma Francis na daya a ziyarar da ya kai kasar Jordan ©REUTERS/Tony Gentile
Talla

Paparoma Francis, wanda ke gabatar da jawabi a birnin Amman, ya bukaci a kawo karshen yakin basasar kasar Syria, sannan kuma a gaggauta samar da dawwamammen zaman lafiya tsakanin Isra’ila da kuma alasdinu.

Bayan ganawarsa da hukumomin kasar ta Jordana yau, an tsara jagoran na cocin Katolika zai gana da dubban ‘yan gudun hijirar kasar Syria da ke zaune a kasar ta Jordan.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.