Isa ga babban shafi
Colombia

Colombia zata dakatar da kai hari kan yan FARC

Shugaban Kasar Colombia Juan Manuel Santos yace sojojin kasar zasu daina kai hari kan ‘Yantawayen kungiyar FARC a yunkurin kawo karshen yakin basasa mafi tsayi a Yankin Amurka ta kudu. A sanarwar da ya yi ta kafar Talabijin, shugaban ya ce ya umurci Ministan tsaron kasar da kwamandojin soji da su daina kai hari kan sansanin ‘yantawayen. 

Shugaban kasar Colombia Juan Manuel Santos
Shugaban kasar Colombia Juan Manuel Santos REUTERS/Efrain Herrera/Presidency-Press
Talla

Akalla mutane 220,000 ne aka kashe a yakin da Dakarun kasar ta Colombia ke yi da ‘yan tawayen FARC masu dauke da muggan makamai.
Santos ya ce akwai alamun da ke nuna cewar a wannan karon kungiyar FARC na nuna goyon bayan shirin gwamnati, na sasantawa a tsakaninsu da kuma samar da zaman lafiya.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.