Isa ga babban shafi
WHO-Zika

WHO ta kaddamar da dokar ta-baci akan Zika

Hukumar lafiya ta duniya WHO ta kaddamar dokar ta-baci domin dakile yaduwar Cutar Zika da ta fi yin illa ga jarirai wadanda ake haifuwa da karamin kai.

Cutar Zika na sa ana haihuwar Jarirai da karamin kai
Cutar Zika na sa ana haihuwar Jarirai da karamin kai REUTERS
Talla

Hukumar Lafiya dai na fuskantar matsin lamba ne kan gano illolin cutar da hanyoyin magance ta, a yayin da ta ke ci gaba da fama da cutar Ebola a kasashen Afrika.

Ana kamuwa da Cutar Zika ne daga cizon sauro kuma yanzu dubban mutane ne cutar ta shafa a watannin da suka gabata a kasashen Latin Amurka.

Tuni dai Hukumar lafiya ta duniya ta yi gargadin cewa za a samu karuwar masu kamuwa da cutar a bana wanda ya zama wajibi a dauki matakan dakile yaduwarta.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.