An kammala taron kasashen duniya kan HIV
An kammala taron kasashen duniya kan cutar Sida a kasar Afrika ta kudu, inda mahalarta taron suka bukaci karin bada tallafi don gudanar da binciken samun maganin cutar wadda yanzu haka ta kama mutane miliyan biyu da rabi a duniya.
Wallafawa ranar:
Shugabar kungiyar masu yaki da cutar mai jiran gado, Linda-Gail Bekker ta ce har yanzu ba a samu nasarar magance cutar ba, duk da kokarin da kasashen duniya ke yi, ganin yadda mutane 15,000 masu fama da cutar suka mutu a cikin kwanaki 5 da aka kwashe ana taron, kuma 1,500 daga cikin su yara kanana ne.
Masana kimiya 15,000 suka halarci taron a Durban don nazari kan cutar da ta hallaka mutane sama da miliyan 30 a cikin shekaru 35 da suka wuce.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu