Isa ga babban shafi
Amurka

Da wuya Amurka ta cika alkawarin Paris

Wani binciken kwararru ya bayyana cewa, akwai yiwuwar Amurka ta gaza cika alkawuran da ta dauka a karkashin yarjejeniyar dumamar yanayi da aka cimma a birnin Paris na Faransa da ziammar rage fitar da hayaki mai gurbata muhalli a kasashen duniya.

An cimma yarjejeniyar Paris ne a cikin watan Disamban bara da zimmar rage yawan fitar da hayaki mai gurbata muhalli, abin da ke barazana ga al'ummar duniya
An cimma yarjejeniyar Paris ne a cikin watan Disamban bara da zimmar rage yawan fitar da hayaki mai gurbata muhalli, abin da ke barazana ga al'ummar duniya REUTERS/Kim Kyung-Hoon/
Talla

Wannan dai na zuwa ne bayan nasarar da Donald Trump ya samu a zaben shugabancin Amurka da aka gudanar a ranar Talata, abin da ya haifar da shakku dangane da makomar yarjejeniyar nan gaba.

To sai kwararrun sun ce, ko da Trump bai soke tsare-tasren shugaba Obama ba kan wannan batu, akwai yiwuwar Amurka ta gaza rage fitar da gurbataccen hayakin nan da shekaru 15 masu zuwa.

A cewar direktan cibiyar yaki da matsalar sauyin yanayi da ke birnin Cologne na Jamus Niklas Hohne, matsalar fitar da hayakin za ta fi tsananta a Amurka matukar Trump ya yi watsi da tsare-taseren shugaba Obama mai barin gado na rage gurbata muhalli.

Amurka dai ta yi alkawarin rage kashi 26 zuwa 28 cikin 100 na hayakin da ta ke fitarwa a yarjejeniyar da ta cimma tare da kasashen duniya a birnin Paris na Faransa a bara.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.