Fafaroma ya nada manyan Limaman Katolika
Fafaroma Francis ya nada manyan Limaman mabiya darikar katolika daga sassan kasashen duniya wadanda ke da alhakin zaben sabon Fafaroma.
Wallafawa ranar:
Uku daga cikinsu Limaman da Fafaroma ya nada Amurkawa ne, yayin da sauran suka fito daga sassa daban daban na duniya.
Sauran Limaman sun fito ne daga kasashen Bangladesh da Belgium da Brazil da Jamhuriyyar Afrika ta tsakiya da Italiya da Mauritius da Mexico da Papua New Guinea da Spain da Venezuela.
Sannan Fafaroman ya yi gargadi ga sabbin Limaman su gujewa abun da zai janyo masu bakin jini tare da kawo baraka a darikar ta Katolika.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu