Da kaina na ke kashe mutane- Duterte
Shugaban kasar Philippines Rodrigo Duterte ya ce, da kansa ya ke kashe mutanen da ake zargi da aikata laifuka a lokacin da ya ke rike da mukamin Magajin Garin Davao.
Wallafawa ranar:
Duterte ya bayyana haka ne a lokacin da ya ke jawabi ga tawagar 'yan kasuwa kan shirinsa na yaki da safarar miyagun kwayoyi wanda yanzu haka, ya yi sanadiyar kashe dubban mutane ba tare da an kai su gaban kotu ba.
Shugaban ya ce, a wancan lokaci da ya ke rike da mukamin Magajin Gari, da kansa ya ke kashe wadanda ake zargin don nunawa 'yan sanda yadda za suyi.
Duterte ya ce, yana hawan babur yana zagaya garin Davoa don neman fitina domin ya kashe mutane.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu