Jam'iyar Shugaban Faransa Macron Na Kan Gaba A Zaben Majalisar Dokoki
Yau aka gudanar da zabukan wakilan majalisar Dokokin kasar Faransa zagaye na farko, inda ake ganin jam'iyar Shugaba Emmanuel Macron na matukar bukatar samun rinjayen wakilai a majalisar.
Wallafawa ranar:
Ma'aikatar Harkokin cikin gida na Faransa ta fadi cewa kashi 40.75 daga cikin dari na masu kuria suka jefa kuri'u a zaben na yau.
Tun bayan samun nasara a zaben shugaban kasa ranar bakwai ga watan jiya bisa abokiyar takarar sa Uwargida Marine Le Pen, Emmanuel Macron ke daukan hankulan jama’a dake son ganin yadda yake taka rawar shugabancin Faransa.
Faransa na da jimillan kujerun wakilan majalisar Dokokin 577 da suka hada da kujeru 11 na wakilai ‘yan kasar Faransa mazauna kasashen duniya.
Tuni dai Jam'iyar Emmanuel Macron ta Republic on the Move ta lashe kujeru 10 daga cikin 11 na mazauna wata kasa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu