Ana Zabukan Kananan Hukumomi Mai Muhimmanci a Kasar Japan
Al’ummar kasar Japan na jefa kuri'a yau Lahadi don zabukan kananan hukumomi wanda sakamakon zaben ke da muhimmanci a kasar inda Gwamnan Babban birnin kasar ke kalubalantar Jamiyyar Firaminista Shinzo Abe wanda farin jininsa ke raguwa.
Wallafawa ranar:
Gwamnan Uwargida Yuriko Koike, wadda tsohuwar mai gabatar da shirye-shirye ce a tashan Talabijin na fatan ganin gamayyar jam'iyun da suka hada kai za su iya kawar da jam'iyar Firaministan dake mulki wato Jamiyyar Liberal Democratic Party, LDP.
Uwargida Yuriko Koike wadda aka zaba Gwamna a bara an sha fadin cewa tana da burin zama Firaministan kasar Japan.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu