Faransa zata taka rawa domin magance rikicin Iraqi
Bisa gayyatar Shugaban Faransa Firaministan Iraki Haider Al Abadi zai kai wata ziyara Faransa ranar 5 ga watan gobe, Shugabanin biyu Emmanuel Macron da Al Habadi za su gana domin tattance hanyoyin da suka dace domin dakile duk wata barrazana da kan iya kawo cikas ga kokarin hukumomin Iraki na sake dawowa da doka da oda a sasan kasar.
Wallafawa ranar:
Kasar Iraqi ta bada umarni dakatar da sauka da tashin jiragen sama a birnin Arbil na yankin Kurdawa, wanda ke a matsayin martani ga zaben raba gardamar balewa daga kasar da kurdawan suka kada.
Hukumomin Bagadaza sun ce zasu ci gaba da matsin lambar tabbatar da cewa kurdawan su mika kai.
Wannan mataki daga hukumomin Bagdaza na a matsayin barrazana ga tattalin arzikin yankin a cewar kakakin ministan sufuri na yankin Kurdawa Oumed Mohamas.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu