Isa ga babban shafi
Iraqi

Macron na neman shiga tsakani a rikicin Kurdawan Iraqi

Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya bukaci gaggauta fara tattaunawa tsakanin gwamnatin Iraqi da Kurdawan da suka nemi kafa kasa mai cin gashin kanta.

Shugaba Emmanuel Macron ya kuma bukaci a bashi dama don shiga tsakanin gwamnatin ta Iraqi da bangaren Kurdawan da nufin kawo karshen takaddamar.
Shugaba Emmanuel Macron ya kuma bukaci a bashi dama don shiga tsakanin gwamnatin ta Iraqi da bangaren Kurdawan da nufin kawo karshen takaddamar. REUTERS/Etienne Laurent/Pool
Talla

Da ya ganawa da Firaministan yankin Nachervan Barzani da mataimakinsa Quobad Talabani, Macron ya bukaci tattaunawa ta fahimtar juna tsakanin bangarorin biyu domin kawo karshen matsalar da ke tsakaninsu.

Baraka ta fito fili tsakanin yankin na Kurdawa da gwamnatin Iraqin ne baya da yankin ya kada kuri'ar raba gardamar ballewa daga kasar, Lamarin da ya sa gwamnatin kasar daukar tsauraran matakai don kaucewa ballewar yankin.

Shugaba Macron ya yi tayin neman damar shiga tsakani don kawo karshe matsalar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.