Za a zurfafa bincike kan amfani da guba a Dhouma
Jami’an hukumar Majalisar dinkin Duniya da ke hana amfani da makamai masu guba za su tono kaburburan mutanen da ake zargin cewa sun mutu ne sakamakon shakar iskan gas mai guba a yankin Douma da ke Syria.
Wallafawa ranar:
Shugaban hukumar Ahmed Uzumcu, ya ce bayan tono gawarwakin mamanta da yawansu ya kai 40, kwararri za su gudanar da gwaje-gwaje domin kawar da shakku kan wannan lamari da ya faru a ranar 7 ga watan afrilun da ya gabata.
Birnin Douma dai birni ne da ke a wajen birnin Damascus inda aka zargi Sojin Gwamnati da amfani da makamai masu guba a kwanakin da suka gabata, harin da ya yi sanadin mutuwar akalla mutane da dama.
Samun rahotannin amfani da makamai masu gubar da aka yi a birnin Douma na Syria a ranar 7 ga watan Afrilu ne ya janyo farmakin hadin guiwa da Amurka da Faransa da Burtaniya suka kai wa Syria a karkashin jagorancin kasar Amurka.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu