Isa ga babban shafi
Chile

Chile na tuhumar limaman Katolik 158 da boye laifukan cin zarafi

Hukumomin Kasar Chile sun ce suna gudanar da bincike kan shugabannin mabiya darikar Katolika 158 da suka hada da Bishop Bishop da masu bushara saboda zargin da ake musu na boye bayanai kan yadda aka dinga cin zarafin yara maza da manya a cocin.

Francis ya bayyana zarge-zargen kan limaman da wani batu da ke kokarin zubar da kimar shugabancinsa.
Francis ya bayyana zarge-zargen kan limaman da wani batu da ke kokarin zubar da kimar shugabancinsa. REUTERS/Stefano Rellandini
Talla

Mai Gabatar da kara, Luis Torres, ya ce binciken ya biyo bayan korafe korafe 144 da aka gudanar da bincike akai da ya shafi mutane 266, cikin su harda yara 178.

Torres ya ce binciken ya faro ne tun daga shekarar 1960, inda aka gano batutuwa da dama masu alaka da cin zarafin Mata, kananan yara dama manyan mabiyan darikar ta Katolika.

Ko a baya-bayan nan sai da shugaban darikar na duniya Fafaroma Francis ya karbi takardun murabus na wasu manyan shugabannin cocin kasar kan makamantan zarg-zargen.

Francis ya bayyana zarge-zargen kan limaman da wani batu da ke kokarin zubar da kimar shugabancinsa.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.