Isa ga babban shafi
New Zealand

An yi Jana'izar wadanda suka mutu a harin Masallacin New Zealand

Yau an gudanar da jana’izar wasu daga cikin mutane da wani dan bindigar ya harbe a Masallatan juma’ar kasar makon jiya, yayin da Firaministar kasar Jacinda Ardern ta bukaci kasashen duniya su hada kai domin daukar mataki kan kafofin sadarwar da ke baiwa masu tsattsauran ra’ayi damar yada manufofin su.

Wannan dai ne harin ta'addanci na farko da kasar ta New Zealand ta taba fuskanta a tarihi
Wannan dai ne harin ta'addanci na farko da kasar ta New Zealand ta taba fuskanta a tarihi REUTERS/Jorge Silva
Talla

Daruruwan mutane da suka hada da Musulmi da ma wadanda ba Musulmi ba ne suka halarci jana’izar a wata makabarta da ke kusa da Masallachin Linwood, daya daga cikin Masallatan da aka kai harin.

Firaminista Jacinda Ardern ta ce ya zama wajibi duniya ta dauki mataki kan kafofin sada zumunta.

A juma'ar da ta gabata ne dai, wani dan bidiga ya bude wuta kan mabiya addinin Islama da ke halartar sallar Juma'a tare da hallaka mutane 49.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.