Isa ga babban shafi
Haiti

An yi yunkurin juyin mulki a Haiti

Ministan shari’ar Haiti Rockefeller Vincent ya ce hukumomin tsaron kasar sun samu nasarar dakile yunkurin wasu gungun mutane na yin juyin mulki.

Shugaban kasar Haiti Jovenel Moïse
Shugaban kasar Haiti Jovenel Moïse AFP / PIERRE MICHEL JEAN
Talla

Vincent yace yayin yunkurin juyin mulkin, gungun mutanen sun yi kokari kashe shugaban kasar ta Haiti Jovenel Moise amma hakarsu bata cimma ruwa ba.

Cikin sanarwar da ya fitar ministan shari’ar na Haiti ya kara da cewar daga cikin masu neman kifar da gwamnatin kasar akwai jami’ai masu rike da manyan mukamai.

Lamarin na zuwa ne a yayin da rikicin siyasa ke neman barkewa sakamakon takaddama kan lokacin karewar wa’adin shugabancin Jovenel Moise.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.