Mutune 25 sun mutu a Haiti lokacin da Fursunoni 400 suka tsere a kurkuku
Hukumomin Haiti sunce, suna neman fiye da fursunoni 200 da suka tsere, kwana guda bayan wani mummunan rikicin a kurkukun da ya yi sanadiyar mutuwar mutane 25 ciki har da darektan gidan yarin.
Wallafawa ranar:
Kamfanin dillancin Labaran Faransa na AFP ta nuna hotonan akalla gawawwaki uku da ke kwance a wajen gidan yarin da kuma wasu fursunonin da aka kame a bayan wata babbar mota, bayan da Kimanin fursunoni 400 suka tsere a ranar Alhamis.
"Daga cikin wadanda aka kashe har da wasu basu ji ba basu gani ba, da fursunonin suka kashe a lokacin da suke tserewa."
Kimanin fursunoni 200 har yanzu ba a gansu ba, amma "'yan sanda na aiki tukuru don ganin an dawo da su. Wasu da dauke da anko, ba za su iya yin nisa ba," in ji jami’in.
Cikin fursunonin da suka mutu harda wani shugaban kungiyar ‘yan daba Arnel Joseph, wanda aka kashe a ranar Juma’a a wani shingen bincike yayin da yake tsewa.
Yayin da yake zaman wakafi kan hukuncin kisan da aka yanke masa, Joseph ya tsere har sau biyu daga wani gidan yari, a Port-au-Prince, a shekarun 2010 da 2017.
A shekarar 2012, aka bude gidan kurkukun mai tsananin tsaro na Croix-des-Bouquets, wanda kasar Canada ta bada tallafi gina shi, na iya ɗaukar fursunoni 872, kodayake an ninka kusan adadin da ke tsare a wurin kafin tserewar na alhamis.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu