Isa ga babban shafi

Yan Taliban sun kwace mulkin Afghanistan

Kungiyar Turai da sauran kasashe na Yammacin Duniya, sun ce yanzu haka suna daukar matakai don kare lafiyar jami’ansu da ke rayuwa a kasar ta Aghanistan, musamman a daidai wannan lokaci da mayakan Taliban suka kwace mulkin kasar.

Yan Taliban a fadar Shugaban kasar Affghanistan
Yan Taliban a fadar Shugaban kasar Affghanistan AP - Zabi Karimi
Talla

Ashraf Gani tsohon Shugaban kasar da ya gudu ,ya ce ya bar kasar ne don kaucewa zubar da jinin fararren hula,yayinda yan Taliban suka kama fadar Shugaban kasar,suna kuma dakon isowar jagororin su daga Qatar.

Tsohon Shugaban Afghanistan Ashraf Ghani
Tsohon Shugaban Afghanistan Ashraf Ghani REUTERS - AFGHAN PRESIDENTIAL PALACE

Tuni kasashen yamma ciki har da Canada, Jamus, Faransa, Amurka da kuma Birtania, suka tsara yadda za su kwashe jami’ansu na diflomasiyya daga kasar.

Tutar Afghanistan
Tutar Afghanistan AFP - ROBERTO SCHMIDT
Amurka ta tallafawa kasar ta Afghanistan da kusan bilyan  88 na dalla wajen samarwa dakarun kasar kayan yaki na zamani tun farkon shekara ta 2002.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.