Isa ga babban shafi
Haiti - Girgizar kasa

Alkaluman mutanen da girgizar kasa ta kashe a Haiti ya kai dubu 1 da 419

Sabbin alkalumma da mahukunta suka fitar na nuni da cewa adadin wadanda suka rasa rayukansu sanadiyyar girgizar kasar da ta afka wa Haiti ranar asabar da ta gabata, a yanzu ya kai mutane dubu daya da 419.

Ana ci gaba da aikin ceto a baraguzan gine-ginen da girgizar kasar Haiti ta rufta.
Ana ci gaba da aikin ceto a baraguzan gine-ginen da girgizar kasar Haiti ta rufta. AFP - STANLEY LOUIS
Talla

Yayin da ake ci gaba da aikin ceto ta hanyar a karkashin tarkacen gine-ginen da suka rufta, zuwa yanzu an tabbatar da cewa sama da mutane dubu 6 da 900 ne suka ramu raunuka, yayin da gidaje dubu 37 suka rushe.

Wasu bayanai na nuna cewa har yanzu akwai sauran mutanen da suka makale a baraguzan gine-ginen da suka rufta, yayinda galibin asibitocin gab da yankin ke makare da masu bukatar agajin gaggawa.

Girgizar kasar mai karfin maki 7 da digo 2 tun a ranakun karshen mako ta afkawa kasar ta Haiti, ko da ya ke ta shafi wasu kasashe makwabta amma tafi barna a cikin Haitin ta yadda ta lalata garuruwa da dama musamman wadanda ke gab da birnin Port-au-Prince da sauran kudancin kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.