Isa ga babban shafi
Afghanistan-Taliban

Facebook ya fara kare jama'ar Afghanistan daga fitinar Taliban

Kamfanin Facebook ya fitar da sabbin matakan tsaro domin kare masu amfani da dandalinsa a Afghanistan bayan mayakan Taliban sun kifar da gwamnatin kasar, yayin da tuni ya dakatar da asusun mayakan.

Wasu daga cikin mayakan Taliban
Wasu daga cikin mayakan Taliban AP - Zabi Karimi
Talla

Kamfanin na Facebook ya dauki matakan ne bayan shawarwarin da ya samu daga masu rajin kare hakkin bil’adama da ‘yan jarida da kungiyoyin fareren hula, yana mai cewa, a yanzu masu amfani da shafin a Afghanistan za su iya boye wallafa-wallafansu ga mutanen da su san su ba.

Kazalika, masu amfani da Instagram mallakin Facebook, su ma za su rika samun sakwannin da ke janyo hankulansu kan yadda za su kare asusunsu a kasar.

Shugaban Sashen Kula da Lamurran Tsaro na kamfanin Facebook, Nathaniel Gleicher ya ce, a halin yanzu suna aiki kafa-da-kafa da takwarorinsu na masana’antun fasaha, da kungiyoyin fararen hula da kuma gwamnati domin bayar da duk wani taimako don kare jama’ar Afghanistan.

Mata na dari-dari wajen amfani da dandalin facebook a Afghanistan.
Mata na dari-dari wajen amfani da dandalin facebook a Afghanistan. OLIVIER DOULIERY AFP/Archivos

Mista Gleicher ya kara da cewa, kamfanin na Facebook ya janye tsarin kustawa cikin runbunan wani aboki domin bibiyar  jerin mutanen da  yake mu’amala da su a shafin a Afghanistan da zummar kare jama’a daga farmakin Taliban musamman ga wadanda mayakan ke fako.

WhatsApp ma dai ya dakile asusun mai magana da yawun Taliban Zabihullah Mujahid.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.