Isa ga babban shafi
Haiti

Majalisar Dinkin Duniya ta tsawaita aikin ta a Haiti da watanni tara

Kwamitin Tsaro na Majalisar Dinkin Duniya ya tsawaita aikin Majalisar a kasar Haiti da watanni tara bayan tattaunawar sa’o’i 11, ya haifar da da mai ido tsakanin mayan kasashen yamma da kuma China.

Sojojin Haiti a watan Oktoban 2021.
Sojojin Haiti a watan Oktoban 2021. Richard PIERRIN AFP
Talla

Kwamitin ya gabatar da wani kuduri na tsawaita wa'adin da kasa da shekara guda kamar yadda Amurka ta nema, amma fiye da watanni shida da China ta bukata.

An kada kuri'ar amincewa da tsawaita wa’adin jim sa'o'i kadan kafin wa'adin aikin siyasa ya kare a kasar, inda aka tsawaita shi zuwa 15 ga watan Yulin shekarar 2022.

Yanzu haka kasar Haiti na cikin matsanancin rikicin siyasa, da tattalin arziki da kuma zamantakewa da tsaro.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.