Isa ga babban shafi

Cutar sarkewar numfaashi da ta bulla a China ba ta kai Covid-19 ba - WHO

Hukumar lafiya ta duniya WHO, ta ce, cutar sarkewar numfashi da aka sake samun bullarta a kasar China, ba ta kai cutar Covid-19 da ke saurin yaduwa ba.

Wasu marasa lafiya da ke karbar kulaawar likitoci a wani aasibiti da da ke kulaa da masu cutar Covid-19 a birnin Shanghai, na kasar China ranar 9 ga watan Janairu, 2023.
Wasu marasa lafiya da ke karbar kulaawar likitoci a wani aasibiti da da ke kulaa da masu cutar Covid-19 a birnin Shanghai, na kasar China ranar 9 ga watan Janairu, 2023. VIA REUTERS - STRINGER
Talla

WHO ta ce har yanzu ba a kai ga gano kwayoyin cutar da suka haifar da irin wannan cuta ba.

Maria Van Kerkhove, mukaddashiyar daraktan sashen kula da cutuka masu yaduwa ta WHO, ta ce karuwar adadin mutanen da ke fama da wannan cuta da ake samu, baya rasa nasaba da raunin garkuwar jiki da kananan yara ke da shi.

Kakakin ma’aikatar lafiya ta kasar China, Mi Feng, ya ce yaduwar cutar sarkewar numfashin da ake samu ga kananan yara, na da nasaba ne da wasu kwayoyin cuta masu kamanceceniya da mura da suke fama da ita.

A makon jiya ne WHO ta bukaci kasar China da ta yi mata cikakken bayani, kan cutar sarkewar numfashin da aka samu labarin cewa tana kama kananan yara, yayin da duniya ta shiga rudani domin fargabar abin da ka iya maimaita kansa na cutar Covid-19.

China da WHO sun fuskanci tambayoyi kan sahihancin rahoton da aka samu game da cutar da ta bulla a Wuhan wato inda Covid-19 ta samo asali a karshen shekarar 2019.

Sai dai rahoton da WHO ta fitar ya tabbatar da cewa, wannan cutar ba za a kira ta a matsayin annoba ba, kamar yadda cutar sarkewar numfashi ta Covid-19 ta addabi duniya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.