Isa ga babban shafi

Isra'ila ta kai sabbin hare-hare a kudancin Zirin Gaza

Isra’ila ta kai sabbin hare-hare ta sama a kudancin Zirin Gaza, inda Falasdinawa ke dauka a matsayin tudun mun tsira, bayan tserewa daga arewacin yankin.

Wasu Falasdinawa yayin aikin ceto wasu da hare-haren Isra'ila ya rutsa da su a garin Khan Younis da ke kudancin Zirin Gaza.
Wasu Falasdinawa yayin aikin ceto wasu da hare-haren Isra'ila ya rutsa da su a garin Khan Younis da ke kudancin Zirin Gaza. © Reuters
Talla

Ya zuwa yanzu alkaluman jami’an lafiya sun nuna cewar adadin fararen hular da suka mutu a hare-haren na daren jiya ya kai mutane 71, akasarinsu mata da yara.

Bayanai sun ce Isra’ila ta kaddamar da jerin farmakin ne a garuruwan Khan Younis, da Rafah da yayi iyaka da Masar, inda ake fatan daga nan za a bayar da damar fara shigar da kayan agaji zuwa Falasdinawa da suka tagayyara, koda yake har yanzu ba a fayyace lokaci ba.

Wasu Falasdinawa a kan iyakar garin Rafah da Masar, yayin kokarin neman damar ficewa daga Zirin Gaza,  16 ga Oktoba, 2023.
Wasu Falasdinawa a kan iyakar garin Rafah da Masar, yayin kokarin neman damar ficewa daga Zirin Gaza, 16 ga Oktoba, 2023. REUTERS - IBRAHEEM ABU MUSTAFA

A wata sanarwa, rundunar sojin Isra'ila ta ce hare-hare sama da 200 ta kai kan kungiyar Hamas cikin daren da ya gabata a fadin zirin Gaza.

A can Isra’ila kuwa, gwamnatin kasar ta ce kimanin mutane dubu 500 aka kwashe daga muhallansu zuwa wasu yankunan, cikin kwanaki goman da suka gabata, bayan farmakin ba-zata mafi muni da mayakan Hamas suka kai mata a ranar 7 ga watan Oktoba.

A wani labarin kuma, kudurin da Rasha ta gabatar wa kwamitin tsaron majalisar dinkin duniya kan neman kiran tsagaita wuta a yakin Isra’ila da Hamas ya gaza samun kuri’u 9 daga cikin 15 da ake bukata kafin amincewa da shi.

Amurka ce dai ta jagoranci yin fatali da kudurin a bisa hujjar cewa, ya bai wa Hamas kariya ta hanyar kin ambaton farmakin da ta kai wa Isra’ila.

Daftarin na Rasha dai ya yi kira ne da a tsagaita wuta tsakanin Isra'ila da Hamas, a kuma saki fursunonin da aka yi garkuwa da su a Gaza, sai kuma bukatar bai wa fararen hula kariya yayin kwashe su zuwa yankunan tudun mun tsira.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.