Isa ga babban shafi
Najeriya

An kai hare haren bama-bamai a Maiduguri

Rahotanni daga birnin Maiduguri dake jihar Borno a Najeriya na cewa, an kaddamar da jerin hare haren bama-bamai a birnin tare da kashe mutane da dama kamar yadda mazauna yankin da kungiyar bada agaji ta Red Cross suka sanar.

Boko Haram ta sha kaddamar da hare hare a garin Maiduguri dake Najeriya.
Boko Haram ta sha kaddamar da hare hare a garin Maiduguri dake Najeriya. AFP PHOTO/STRINGER
Talla

An dai kai hare haren ne a daren jiya talata a yankin Ajilari, inda aka kai munanan hare hare a cikin watan satumban da ya gabata, da ya hada da na ranar 20 ga watan,wanda ya kashe mutane akalla 117.

An dai dora alhakin kai wancan harin akan mayakan Boko Haram da ke ci gaba da kai farmaki kan fararan hula a yan kwanakin nan.

A cikin watan da ya gabata ne kungiyar kare hakkin adam ta Amnesty International ta ce, rikicin Boko Haram ya yi sanadiyar mutuwar mutane akalla dubu 1 da 600 tun daga watan Yunin da ya gabata a Najeriya da Nijar da Chadi da Kamaru.

Amnesty dai ta bukaci hukumomi da su dauki matakan kare lafiyar farararn hula da hare haren ke ritsa wa da su.

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.