Isa ga babban shafi
Najeiya-Boko-Haram

BOKO HARAM: Mutane 22 sun Mutu a Borno

Akalla mutane 22 suka rasa rayukansu a wani harin kunar bakin wake da aka kai cikin Masallacin kauyen Umarari da ke Jihar Borno, a dai-dai lokacin Sallar Asuba.

Boko Haram na cigaba da zama barazana a arewacin Najeriya
Boko Haram na cigaba da zama barazana a arewacin Najeriya AFP PHOTO
Talla

A cewar hukumomi Jihar ta Borno harin Umarari dake da tazaran kilomita 5 daga birnin Maiduguri ya kuma jikkata wasu 32.

Wannan harin shine irin sa na farko a Borno tun bayan harin da aka kai sansani ‘yan gudun hijira dake Dikwa tare da kashe mutane 50.

A cewar wani Jami’an rundunar sa kai ta fararan kaya Alhaji Danbatta, maharan su biyu, sun kutsa kai cikin masallaci a dai-dai lokacin da ake jam’in Sallah kana ya tada bam din dake jikinsa.

Jihar Borno dake yawaita fuskantar hare-haren Mayakan Boko Haran, Rundunar sojin Najeriya na ikirarin kakkabe mayakan daga kauyukan jihohin.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.