Saraki ya koma kotu a yau jumma'a
Shugaban majalisar dattawan Najeriya, sanata Bukola Saraki ya isa kotun ladabtar da ma’aikata a yau jumma’a, inda ya ke fuskantar shari’a akan zarge zargen da ake yi masa na bayar da bayanan karya game da kadarorin da ya mallaka da kuma cin hanci da rashawa.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Kokarin Mr. Saraki na kaucewa tuhumar ya ci tura, bayan kotun kolin kasar ta ce, kotun ladabtar da ma'aikatan na da hurumin tuhumar sa.
A makon jiya ne, kotun ta dage karar zuwa yau jumma’a kuma ya isa kotun da misalin karfe 9:54 agogon kasar yayin da lauyan da ke kare shi ke cewa, za su yi nasara.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu