Isa ga babban shafi
Najeriya - Ta'addanci

Mayakan ISWAP sun kashe dakarun Najeriya 18 a Maiduguri

Akalla sojojin Najeriya 16 mayakan k’ungiyar ISWAP suka  kashe lokacin suka y iwa tawagar motocinsu kwanton bauna a jihar Borno.

Dakarun Najeriya da ke yaki da ta'addanci.
Dakarun Najeriya da ke yaki da ta'addanci. Getty Images
Talla

Harin na ranar Laraba shine mafi muni da k’ugiyar ISWAP ta kai a kan sojojin Najeriya a cikin wannan shekarar tun da aka fara hare haren ta’adanci.

'Yan kugiyar IS din dai sun tada bama bamai tare da budewa rundunar sojin wuta ne yayin da suke kan hanyar dake tsakanin Maiduguri  da Mangono, abin da ya yi sanadiyar mutuwar sojoji 18 da ‘yan sa kai guda 2, yayin da mayakan  suka yi garkuwa da sojoji 2.

Sha daya daga cikin tawagar sojojin sun jikkata a harin, sannan motocin su da dama aka kona, a cewar wani soja da ya nemi a sakaya sunansa saboda rashin ba shi da izinin zantawa da manema labarai ba.

Tuni kungiyar ISWAP ta dauki alhakin kai harin kuma ta ce sojoji 25 ta kashe a cewar masu bibiyar kafarsu

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.