Isa ga babban shafi

INEC ta yi taron kintsawa zaben gwamnoni a Najeriya

Hukumar zabe a tarayyar Najeriya tayi zama da dukkan masu ruwa da tsaki a harkar tsaro domin kintsawa zaben gwamnoni da ‘yan majalisun jihohi da za’a gudanar a ranar asabar 18 da watannan. 

Shugaban hukumar INEC farfesa Mahmud Yakubu kenan, lokacin da yake karbar sakamakon jihohi na zaben shugabancin kasar da aka yi ranar 25 ga watan Fabrairu, 2023.
Shugaban hukumar INEC farfesa Mahmud Yakubu kenan, lokacin da yake karbar sakamakon jihohi na zaben shugabancin kasar da aka yi ranar 25 ga watan Fabrairu, 2023. AP - Ben Curtis
Talla

Wannan na zuwa ne, bayan kwanaki da INEC din ta kara wa'adin mako guda na zaben gwamnoni da 'yan majalisun jihohin kasar, sakamakon abin da ta kira na sake fasalta na'urorin tantance masu kada kuri'a wato BVAS.

A ranar 25 ga watan Fabrairu ne aka gudanar da zaben shugaban kasa da na 'yan majalisun tarayya a Najeriya, inda Bola Ahmed Tinubu na jam'iyyar APC ya lashe zaben.

Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken rahoton da Muhammad sani Abubakar ya hada, daga Abuja.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.