Isa ga babban shafi

Najeriya: Kotuna sun raba 'yan majalisan Tarayya 31 da kujerun su kawo yanzu

Kotunan da ke sauraron shari’ar zabe a Najeriya sun gabatar da hukunce hukunce daban daban a baya-bayan nan wadanda suka raba ‘yan majalisun tarayya 31 da kujerun su.

Zaman sauraren kararrakin zaben shugaban kasa a Abuja. 06/09/23
Zaman sauraren kararrakin zaben shugaban kasa a Abuja. 06/09/23 AP - Olamikan Gbemiga
Talla

Daga cikin mazabun da aka soke wadannan zabukan ‘yan majalisun tarayya, akwai mazabun Kogi ta Gabas da Kogi ta Tsakiya, sai kuma Delta ta Tsakiya da Delta ta Kudu tare da kujerar Filato ta kudu. 

Yayin da kotu ta bukaci gudanar da zabuka a wasu yankuna na kujerun Kogi ta Gabas da Delta ta Kudu da kuma Delta ta Tsakiya, kotun ta kuma mikawa ministan kwadago Simon Bako Lalong kujerar Sanatan Filato ta Kudu. 

Ga jerin ‘yan majalisun wakilan da suka rasa kujerun su da kuma jam’iyyun da suka fito: 

Umar Ysuuf Datti – NNPP, Kano 

Amobi Ogah – LP , Abia 

Fred Agbedi – PDP, Bayelsa 

Ngozie Okolie – LP, Delta 

Umar Yerima – NNPP, Kano 

Ikenga Ugochinyere – PDP, Imo 

Chijioke Okereke – LP, Enugu 

Seyoi Sowunmi – LP, Lagos 

Aminu Chindo – PDP, Katsina 

Ismaila Dalha – PDP, Katsina 

Peter Gyandeng – PDP, Filato 

Munachim Alozie – LP, Abia 

Ibe Osunwa – LP, Abia 

Francis Waive – APC, Delta 

Joshua Gana – PDP, Niger 

Emeka Nnamani – LP, Abia 

Jonathan Ukodhiko – PDP, Delta 

Idris Dankawa NNPP, Kano 

Adamu Yakubu – NNPP, Jigawa 

Thaddeus Atta – LP, Lagos 

Dachung Musa Bagos – PDP,Filato 

Beni Lar – PDP, Filato 

Sunday Umeha – LP, Enugu 

Mohammed Jamilu – PDP, Katsina 

Ilyasu Abubakar – PDP, Katsina 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.