Isa ga babban shafi
Nijar

Boko Haram: Nijar ta kafa dokar ta baci a Diffa

Gwamantin Jamhuriyar Nijar ta kafa dokar ta baci a yankin Diffa inda kungiyar Boko Haram ta kashe akalla mutane 40 a 'yan makwannin da suka gabata.

Kasashen Yankin tafkin Chadi sun kafa runduna domin yaki da Boko Haram.
Kasashen Yankin tafkin Chadi sun kafa runduna domin yaki da Boko Haram. REUTERS/Stringer
Talla

Dokar ta kwanaki 15 za ta bai wa hukumomin kasar damar karfafa matakan tsaro da hana fita da kuma taikata zirga-zirgar mutane da kuma hana safarar kayayyakin abinci kamar yadda gwamnatin ta sanar ta kafar talabijin.

Gwamantin dai ta dau irin wannan matakin a watan Fabairun da ya gabata.

Akalla ‘yan gudun hijira dubu 150  da rikicin Boko Haram a Najeriya ya tilasta wa kauracewa gidajensu, suka samu mafaka a yankin Diffa, yayinda a cikin watanni 8 da suka gabata, kungiyar ta kai hare hare sau 57 a yankin kamar yadda wata kididdigar ta Majalisar dinkin duniya ta nuna.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.