Isa ga babban shafi

Wani bam da aka dana a gefen hanya ya kashe mutane a Nijar

Wani bam da aka dana a gefen hanya ya kashe wasu mutane biyu tare da jikkata wani guda a kudu maso gabashin Jamhuriyar Nijar a ranar Lahadi.

Sojojin Nijar yayin sintiri a iyakar kasa da Nigeria.
Sojojin Nijar yayin sintiri a iyakar kasa da Nigeria. REUTERS/Luc Gnago
Talla

Wani mazaunin yankin ya bayyana cewa wadanda suka rasa rayukan nasu mata ne, wadanda suke wucewa da jakunan su ta kusa da inda aka dana bam din a kusa da garin Bosso da ke yankin Diffa.

Bosso da ke gabar tafkin Chadi, yanki ne da ake yawan fuskantar hare-haren 'yan ta’adda masu ikirarin jihadi, ciki har da mayakan Boko Haram da abokan hamayyarsu ‘yan ISWAP.

A watan da ya gabata, wasu da ake zargin mayakan Boko Haram ne suka harbe manoma 11 a Diffa, kamar yadda wani jami’in yankin ya tabbatar.

Jamhuriyar Nijar na daga cikin kasashen da suke fama da hare-haren ‘yan ta’adda a yankin Sahel, wadanda suka fara tayar da kayar baya a kasar Mali cikin shekarar 2012, daga bisani kuma suka fantsama zuwa makwaftan kasashe.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.