Isa ga babban shafi
Ukraine

Rikici ya barke a kudancin Ukraine

Rikici ya barke a garin Odessa da ke kudancin Ukraine tsakanin ‘Yan sanda da dubban mutanen kasar da ke kishin Rasha, a yayin da gwamnati ke zargin Rasha da kokarin tarwatsa Ukraine.

Daruruwan masu zanga-zanga a kasar Ukraine
Daruruwan masu zanga-zanga a kasar Ukraine REUTERS/Gleb Garanich
Talla

‘Yan sanda sun yi arangama ne da dubban mutanen Ukraine da ke kishin Rasha, kuma an samu hasarar rayukan mutane da dama.

Kusan wannan arangama a garin Odessa, ta bude wani sabon babin rikici ne, a daidai lokacin da hukumomin Ukraine ke kokarin dakile tarzomar da ta addabi gabacin kasar.

Ganin haka ne kuma yasa Fira Minista Arseniy Yatsenyuk, ya zargi Rasha da yunkuri ruguza kasar Ukraine bayan ta amince da Crimea da suka amince su koma ikon Rasha.

Masana siyasa a Turai sun bayyana fargaba akan Ukraine na dab da fadawa yakin basasa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.