Isa ga babban shafi
Faransa-India

Cinikin jiragen yaki zai inganta huldar India da Faransa

Yarjejeniyar cinikin jiragen yaki 36, da India ta kulla da Faransa za ta kara inganta huldar diflomasiyya tsakanin kasashen biyu  

Firaministan India Narendra Modi tare da Shugaban Faransa Francois Hollande
Firaministan India Narendra Modi tare da Shugaban Faransa Francois Hollande REUTERS/Charles Platiau
Talla

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da kasahen ke fafutukar farfado da tattalin arzikinsu

 

 

Firaministan India, Narendra Modi a ziyarsa ta farko da ya kai kasar Faransa, ya bayyana cewa, ya bukaci mallakan jiragen yakin faransa 36 ne, kirar Rafel Jet domin su maye guraben jiragen yakin India da suka tsufa.

A shekara ta 2012, kasashen na India da Faransa sun kulla yarjejeniyar cinikin jiragen yaki, to sai dai hakarsu ba ta cimma ruwa ba, yayin da masana ke ganin cewa sabuwar yarjejeniyar ta wannan karan za ta kawo karshen cece kuce game da yarjejeniyar farko.

A danyan bangaren kuwa, yarjejeniyar cinikin na zuwa ne, a dai dai lokacin da Modi ke kokarin janyo hankulan masu saka hannnayen jari a kasarsa daga nahiyar turai, yayin da kuma yake fafutukar farfado da martabar India a idan Turai dangane da harkar kasuwanci.

Shi dai Shugaban Faransa Francois Hollande ya bayyana cewa kasashen biyu za su ci gaba da hulda mai tasiri
.

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.