Masu zanga zanga sun yi barna a Jamus
Hukumomin kasar Jamus sun bayyana cewa daruruwan jama’a sun lalata gine gine ta hanyar jefe jefe a birnin Leipzig dake gabashin Kasar a lokacin wata zanga zanga
Wallafawa ranar:
Ana ganin cewa, zanga zangar nada nasaba da taron G7 da manyan kasashen duniya masu karfin tattalin arziki za su gudanar a gobe lahadi.
Majiyar yan sandan Kasar ta ce, jami’an yan sanda uku ne suka samu raunuka sakamakon zanga zangar yayin da suka yi nasarar cafke mutun daya daga cikin masu boren.
Majiyar ta kara da cewa masu zanga zangar nata kona tayoyi a tsakiyar birnin na Leipzig. To sai dai tuni hukumomin Kasar suka fara gudanar da bincike domin gano hakikanin abinda ya tunzura jama’a har suka yi bore.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu