Isa ga babban shafi
Rasha

Tarayyar Turai ta tsawaitawa Rasha takunkumi

Kungiyar Tarayyar Turai ta tsawaita takunkuman kariyar tattalin arziki da ta kakaba wa Rasha sakamakon rawar da kasar ke takawa a rikcin Ukraine.

Shugaban Rasha Vladimir Putin
Shugaban Rasha Vladimir Putin REUTERS/Sergei Karpukhin
Talla

Mambobin Kasashe 28 a majalisar kungiyar wadanda suka gudanar da taro a birnin Brussels, sun ce Rasha ta ki mutunta yarjejeniyar sulhun da aka kulla tsakaninta da Ukraine da kuma ‘yan aware a birnin Minsk domin kawo karshen wannan rikici, saboda haka ya zama wajibi a tsawaita takunkuman da aka sanya wa kasar.

Kungiyar Turai ta ce ta lura shekara ta 2015 na gaf da kawo karshe ba tare da Rasha ta canza matsayi a game da irin rawar da ta ke takawa a gabashin Ukraine ba, kuma a irin wannan yanayi ba makawa face tsawaita takunkuman karya tattalin arziki a kanta.

Sai dai a wata sanarwa da ta fitar jim kadan bayan sanar da matakin na Tarayyar Turai, ma’aikatar harkokin wajen Rasha, ta bayyana takaicinta a game da yadda kungiyar ta kawar da kai a game da matsalar ta’addanci wadda ita ce babbar barazana a cewarta, inda a maimakon haka Turai ta zabi tsawaita takunkuman.

Kafin nan dai Firaministan Rasha Dmitry Medvedev, ya ce za su tsawaita takunkumai na tattalin arziki a kan kasar Ukraine saboda kasar ta zabi yin huldar kasuwanci da Turai a maimakon Rasha.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.