Isa ga babban shafi
Faransa

An abkawa Musulmi a Masallaci a Faransa

Wasu gungun masu zanga-zanga a Faransa sun abkawa wani masallaci tare da Kona Al Qur’ani mai tsalki a yankin Ajaccio. Lamarin ya faru ne da yammacin jiya Juma’a bayan an kashe wasu ‘Yan Sanda da jami’an kashe gobara guda biyu a yankin Jardins de L'Empereur.

Wajen da musulmi suka kebe suna ibada a Ajaccio da aka lalata a Faransa
Wajen da musulmi suka kebe suna ibada a Ajaccio da aka lalata a Faransa Reuters/ PIERRE-ANTOINE FOURNIL
Talla

Mutane sama da 150 suka hada gangami domin nuna goyon baya ga ‘Yan sanda bayan kashe jami’ansu guda biyu.

Amma daga baya kuma wasu daga cikin masu zanga-zangar suka abkawa Masallaci suna fadin Larabawa su fice kasarsu tare da farfasa kofa da tagogin masallacin da kuma kona wani sashe na Al Qur’ani mai tsarki.

Gwamnatin Faransa dai ta yi allawadai da al’amarin wanda ta danganta a matsayin nuna wariya da kyamar baki.

Jam’iyyar ‘Yan kishin kasa ce ta Marine Le Pen mai adawa da bakin haure ta lashe zaben kananan hukumomi da aka gudanar a yankin Corsica inda aka kai wa musulmin harin a jiya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.