Isa ga babban shafi
Faransa

Hollande zai gana da Paparoma

Fadar shugaban kasar Faransa tace shugaba Francois Hollande zai gana da Paparoma Francis a wannan mako kan kisan da aka yiwa shugaban mabiya darikar katolika a kasar. 

Mabiya darikar Katolika a Faransa
Mabiya darikar Katolika a Faransa CHARLY TRIBALLEAU / AFP
Talla

Ziyarar da Hollande zai kai fadar Vatican gobe Laraba ita ce zata zama ta biyu a tun bayan zamansa shugaban kasar Faransa.

Sai dai fadar shugaban ba tayi karin haske kan abinda shugabannin biyu zasu fi maida hankali wajen tattaunawa ba.

A ranar 26 ga watan Yulin da ya gabata Adel Kermiche da Abdel Malik Petijean suka kutsa kai cikin dakin bauta a Faransa inda suka yanka wanishugaban darikar Katolika a gaban mabiyansa.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.