Isa ga babban shafi
Hungray

Luxembourg ta bukaci korar kasar Hungary daga Tarayyar Turai

Ministan harkokin waje na kasa Luxembourg Jean Asselborn, ya bukaci kungiyar tarayyar turai EU ta kori kasar Hungary daga cikinta.

Wasu masu gudun hijira da ke zanga zanga dangane da wulakancin da suke fuskanta daga mahukuntan kasar Hungary
Wasu masu gudun hijira da ke zanga zanga dangane da wulakancin da suke fuskanta daga mahukuntan kasar Hungary Reuters/路透社
Talla

Asselborn ya ce kiran yazama dole idan akayi la’akari da yawaitar sabawa dokokin tarayyar turan da kasar ta Hungary ke yi.

Asselborn ya ce saba ka’idojin sun kunshi, wulakanta masu gudun hijira, tauye bangaren Shari’ah na kasar da kuma rashin bawa kafafen yada labarai cikakken ‘yanci.

Sai dai kuma Ministan Harkokin wajen na Hungary Peter Szijjarto ya maida martanin cewa, kiran suka ne kawai marar ma’ana ake yi ga kasarsa.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.